Tag: Gwamna

  • Mutumin Da Ya Yi Tattaki A Yankin Kudu Ya Samu Kyautar Naira Milyan Goma Daga Gwamna

    Wani mutum dan asalin jihar Ebonyi mazaunin jihar Lagos mai suna Comrade Jeremiah Obaji, wanda ya yi tattaki na tsawon kwanaki 17 daga Ikorodu dake jihar Lagos zuwa garin Abakaliki domin godewa Gwamna Francis Nwifuru kan yadda yayi silar dawowar zaman lafiya a yankin Effium, ya samu kyautar Naira Miliyan Goma daga wajen Gwamnansu na jihar Ebonyi.

    Mutumin dai yayi tafiyar kusan kilomita 600 ne a kafa, a tsawon kwanaki 17 da yayi a hanya sannan kuma ya samu kyakkyawar tarba a wajen jama’ar gari.

    koMutumin Da Ya Yi Tattaki A Yankin Kudu Ya Samu Kyautar Naira Milyan Goma Daga Wajen Gwamnansu

    …ko a cikin masu tattaki a Arewa sun taba samun irin wannan kyautar?

    Dan asalin jihar Ebonyi mazaunin jihar Lagos Comrade Jeremiah Obaji, wanda ya yi tattakin tsawon kwanaki 17 daga Ikorodu dake jihar Lagos zuwa garin Abakaliki domin godewa Gwamna Francis Nwifuru kan yadda ya yi silar dawowar zaman lafiya a yankin Effium, ya samu kyautar naira milyan goma daga wajen Gwamnansu na jihar Ebonyi.

    Mutumin dai ya yi tafiyar kusan kilomita 600 ne a kafa, a tsawon kwanaki 17 da ya yi a hanya. Sannan kuma ya samu kyakkyawar tarba a wajen jama’ar gari.Mutumin Da Ya Yi Tattaki A Yankin Kudu Ya Samu Kyautar Naira Milyan Goma Daga Wajen Gwamnansu

    …ko a cikin masu tattaki a Arewa sun taba samun irin wannan kyautar?

    Dan asalin jihar Ebonyi mazaunin jihar Lagos Comrade Jeremiah Obaji, wanda ya yi tattakin tsawon kwanaki 17 daga Ikorodu dake jihar Lagos zuwa garin Abakaliki domin godewa Gwamna Francis Nwifuru kan yadda ya yi silar dawowar zaman lafiya a yankin Effium, ya samu kyautar naira milyan goma daga wajen Gwamnansu na jihar Ebonyi.

    Koh a cikin masu tattaki a Arewa akwai wanda ya taba samun irin wannan kyautar?

  • Bala Wunti Ya Karyata Maganar Tsayawa Takarar Gwamna a Bauchi, Yace Yana Cigaba da Tuntuba

    Dr. Bala Wunti ya bayyana cewa bai taba ayyana tsayawa takarar Gwamnan Bauchi ba, sabanin jita-jitar da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa ya amince zai tsaya takara a 2027.

     

    A cikin wata sanarwa da ya fitar, Dr. Wunti ya ce: “Ina matuƙar godiya ga kiraye-kiraye da dama da al’umma ke yi na shiga siyasa, amma a halin yanzu ina ci gaba da tuntuba da muhimman shugabanni. A lokacin da ya dace zan bayyana matsayina na a hukumance.

     

    Ya kara da cewa duk wata sanarwa daga gare shi za a fitar ta ne ta hanyar shafukan sada zumunta na hukuma da aka tabbatar da sahihancinsu, tare da jan hankalin jama’a cewa babu wanda ya samu izinin yin magana a madadinsa.

     

    Dr. Bala Wunti ya gode wa duk masu kawo wannan batu a gareshi tare da yi wa jihar Bauchi da al’ummarta fatan alkhairi.