Tag: Kotu

  • DA DUMI-DIMI: Kotun Bauchi Ta Baiwa EFCC Damar Ci Gaba da Binciken Hamza Koshe da Kamfaninsa

    Alkalin Babbar Kotun Jiha dake Bauchi, Mai Shari’a Aliyu Baba Usman, ya baiwa Hukumar (EFCC) damar ci gaba da bincike a kan Alhaji Hamza Koshe da kamfaninsa mai suna Pentech Engineering Nig. Ltd.

     

    Rahotanni sun bayyana cewa a ranar 23 ga Satumba, 2024, Koshe ya shigar da kara a kotu yana neman a hana EFCC ta ci gaba da bincike da gurfanar da shi tare da kamfaninsa.

     

    Yayin yanke hukunci a ranar 30 ga Yuli, 2025, Mai Shari’a Usman ya bayyana cewa: “Wannan kotu da sauran kotunan shari’a ba su da hurumin hana hukumomin tsaro da doka gudanar da ayyukansu na bincike da gurfanarwa, musamman a kan laifukan rashawa, almundahana, halatta, da sauran manyan laifukan tattalin arziki.”

     

    Saboda haka, kotu ta baiwa EFCC damar ci gaba da bincike a kan Koshe.

     

    Tun da farko EFCC ta gayyaci Koshe domin amsa tambayoyi, amma maimakon ya amsa, sai ya garzaya kotu ya shigar da kara.

     

    Zamani TV