Rundunar ’Yan Sanda ta Kaduna Ta Ce Tsohon Gwamna El-Rufai Ya Shigo Da ’Yan Daba Da Suka Tarwatsa Taron Siyasa

Written by

in

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa ta kaddamar da bincike kan wani taron siyasa da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai ya shirya, wanda ya rikide zuwa tashin hankali da harbe-harbe.

SaharaReporters ta ruwaito cewa wasu ’yan daba da ake zargin gwamnatin jihar ta dauko su sun kai farmaki a wurin taron hada kan jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da African Democratic Congress (ADC) a cikin garin Kaduna, inda suka jikkata mutane da dama.

Rahotanni sun nuna cewa taron hadin gwiwar jam’iyyun SDP da ADC karkashin jagorancin Malam Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan jihar, shi ne ya rikide zuwa tashin hankali har ya haifar da tarzoma da harbe-harben bindiga.

Comments

Leave a Reply