Category: Breaking News

  • What a Coincidence! Elected Senator in 2007, Set to Return to the Senate in 2027, God Willing – Kauran Bauchi: By Hon Hafiz Maiauduga, PhD. CPMC. Part 4

    History often presents societies with unique opportunities to reconnect with their glorious past while shaping a brighter future. For the people of Bauchi South Senatorial District, the year 2027 represents one such historic moment.

    In 2007, the people of Bauchi South overwhelmingly entrusted Senator Bala Abdulkadir Mohammed, CON, Kauran Bauchi, with the mandate to represent them in the Senate of the Federal Republic of Nigeria. Twenty years later, in 2027, history beckons once again (Bi’iznillah).

    The coincidence of 2007 and 2027 is more than a mere alignment of dates; it symbolizes a return to tested leadership, experience, and effective representation. Over the past two decades, Kauran Bauchi has continued to distinguish himself in public service, first as Senator, then as Minister of the Federal Capital Territory, and presently as Governor of Bauchi State, where he has recorded remarkable achievements in infrastructure, education, healthcare, agriculture, and human development.

    As Bauchi South prepares for the 2027 General Elections, there is a growing conviction that history should indeed repeat itself by returning Kauran Bauchi to the Senate. His vast experience, national influence, and proven commitment to the welfare of the people make him uniquely qualified to effectively champion the aspirations of Bauchi South at the national level.

    The year 2027 therefore offers the people of Bauchi South an opportunity not only to make history but also to reward visionary leadership and ensure continuity in quality representation.

    Indeed, after two decades, the message resonates louder than ever: History Shall Repeat Itself—2007 and 2027, Back to the Senate Kauran Bauchi.

    HON. HAFIZ MAIAUDUGA, PhD. CPMC.

    Sunday 12 July, 2026.

  • YANZU-YANZU: Kotu ta wanke dan sanda Abba Kyari daga gaba daya tuhume-tuhumen da ake masa

    Mai Shari’a James Omotosho na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ya sallami tare da wanke dakatararren Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Abba Kyari, daga tuhume-tuhume guda 23 na zargin rashin bayyana kadarori da Hukumar National Drug Law Enforcement Agency (NDLEA) ta shigar a kansa.

    An gurfanar da Mista Kyari tare da ‘yan’uwansa guda biyu, inda ake zarginsu da rantsuwa kan takardun shaida na karya domin ɓoye asalin wasu kadarori.

    A cikin hukuncinsa, Mai Shari’a Omotosho ya bayyana cewa NDLEA ta gaza gabatar da isassun hujjoji da za su tabbatar da zarge-zargen, musamman dangane da batun rashin bayyana filayen kadarori.

    Kotun ta ce tabbatar da mallakar fili na iya samuwa ta hanyar tarihin gargajiya, takardun mallaka, ayyukan mallaka ko kuma mallaka ta alaƙa, amma masu gabatar da ƙara ba su gabatar da ko ɗaya daga cikin waɗannan hujjoji ba domin nuna cewa kadarorin da ke Fountain Estate, Kasana, mallakin Abba Kyari ne, duk da cewa an ce na Ramatu Kyari ne.

    Haka kuma, kotun ta ce babu wata hujja mai ƙarfi da ta danganta Kyari da wasu kadarori da ke kan titin Linda Choko a Asokoro da kuma a Maiduguri, Jihar Borno.

    A nasa ɓangaren kare kai, Kyari ya bayyana cewa kadarorin da ke Borno mallakin mahaifinsa ne wanda ya bari masa da ‘yan’uwansa a matsayin gado, kuma masu gabatar da ƙara ba su iya karyata wannan ba.

    Kotun ta kuma ce an tuhumi ‘yan’uwan Kyari da laifin haɗa baki ne ba tare da hujja mai ƙarfi ba, lamarin da ya nuna rashin gaskiya a shari’ar.

    A ƙarshe, kotun ta bayyana cewa shari’ar NDLEA ba ta da ƙarfi, tare da sallamar dukkanin waɗanda ake tuhuma.

    An bayyana cewa wanda ake tuhumar ya yi wa ƙasa hidima tsawon lokaci, don haka bai kamata a ci gaba da tsananta masa ba.

  • Residents of Styre Quarters, Zango behind IDC in Bauchi Local Government Area of Bauchi State have continued to call on governments at all levels to come to their aid.

    The residents say they are disturbed by the lack of an access road to their homes, especially during the rainy season, due to the condition of a local bridge in the area which is currently inaccessible.

    The bridge was washed away in 2025 after a heavy downpour, leaving motorists stranded and unable to access their homes.

    As a result, residents have had to improvise by taking a longer route through the Bauchi Furniture Company–Gudun area before connecting to another road that leads to their homes.

    Abdulqadir Bala, a resident of the community, described the situation as devastating and disturbing.

    “We don’t know what to do because we called on the government to help us, but up till this time nothing has been done. This is what we have been fearing, and thank God no life was lost when the bridge was washed away,” he said.

    Another resident, Muhammad Ibrahim, attributed the incident to a lack of good governance.

    “If we had a responsible government that cares about its people, such a thing would not happen. If we had politicians in this area, we wouldn’t have been in such a situation. But God is watching, and one day everything will be over,” he said.

    Zamani TV reporter Aminu Harsanu Guyaba contacted the Chairman of Bauchi Local Government Area, Mahmud Babamaji, to inform him about the situation in Styre Quarters. He responded:

    “Thank you for reaching out to me. As a government, we will do everything possible to help them. We will write to the authorities concerned.”

    Despite the chairman’s assurance, the community says it is yet to receive a delegation from the local government secretariat to inspect the damaged bridge and commiserate with residents affected by the flood.

    Zamani TV gathered that within three months September, October, and November 2025 the Bauchi Local Government Area received a FAAC allocation of ₦3,150,154,526.14.

    However, the community is still struggling to have its bridge repaired by the government, but residents are making efforts to repair it by contributing money to have an alternative.

  • Majalisa ta amince a ƙirƙiro jihohi shida a Najeriya

    Haɗaɗɗiyar kwamitin majalisar dattawa da ta majalisar wakilai ta tarayya kan gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya ta amince da buƙatar ƙirƙirar sabbin jihohi guda shida a faɗin ƙasar.

    Wannan matsaya ta fito ne a ƙarshen taron ƙara wa juna sani na kwana biyu da aka gudanar a jihar Legas, ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, tare da mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu.

    A cewar rahoton jaridar Daily Trust, kwamitin ya tattauna ne kan buƙatu 69 da suka haɗa da ƙirƙirar jihohi 55 da kuma ƙananan hukumomi 278.

    Daga cikin waɗannan buƙatun, kwamitin ya amince da ƙirƙirar jihohi shida — ɗaya daga kowace shiyya ta ƙasar — a matsayin matakin farko kafin amincewar cikakkiyar majalisa da kuma gudanar da sauran matakai na doka.

    Da zarar aka amince da wannan shawarwarin gaba ɗaya, adadin jihohin Najeriya zai ƙaru daga 36 zuwa 42 jihohi.

  • ‘Yan Sanda Sun Cafke Wanda ake Zargi da Kashe Mawakin Gargajiya

    ‘Yan sanda a ƙaramar hukumar Tafawa Balewa ta jihar Bauchi sun kama wani mutum da ake zargi da hannu a kisan fitaccen mawaki, John Zuya Zuya, wanda ya shahara a tsakanin al’ummar Sayawa.

    Rahotanni sun bayyana cewa marigayin ya rasu ne bayan dawowarsa daga Lagos, inda ya gudanar da wani gagarumin bikin nishadi tare da masoyansa.

    Ana zargin wani abokinsa mai suna Emmanuel Wakili da kisan, bisa rahotannin da ke cewa an samu sabani tsakaninsu saboda kishi.

    Hukumar ‘yan sanda ta tabbatar da cewa bincike na ci gaba domin gano cikakken abin da ya faru.

  • Shekaru Biyu Na Cigaba a Bangaren Albarkatun Kasa a Jihar Bauchi

    Jihar Bauchi ta cika shekaru biyu da aiwatar da gagarumin sauyi a bangaren harkokin albarkatun kasa, inda aka samu labarin sabuwar tafiya mai cike da hangen nesa, sauye-sauyen manufofi da kuma jarin da bai taba kasancewa ba a baya. A tsakiya na wannan tafiya akwai Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Daular Usmaniyya), tare da wakilinsa a bangaren, Kwamishinan Habbankunan Halittu, Hon. Muhammad Maiwada Bello.

    Tun daga nada shi a watan Agusta 2023, Hon. Maiwada Bello ya kawo sabon salo a tsarin kula da albarkatun kasa a matakin jiha, inda aka farfado da bangaren da aka taba dauka marar amfani, zuwa daya daga cikin ginshikan bunkasar tattalin arzikin jihar, janyo jarin waje da kuma ci gaban mutane.

    A watan Afrilu 2025, Ma’aikatar ta shirya taron horas da ma’aikata na tsawon mako biyu a Hotel Zaranda, inda aka koyar da sabbin dabarun hakar ma’adinai. Haka kuma gwamnati ta sayi kayan aiki na zamani da motoci guda hudu domin bunkasa ayyukan BOGAA da BAMSEL.

    Har ila yau, an dauki sabbin ma’aikata 19 a BAMSEL/ma’aikatar da kuma 43 a Bauchi Oil & Gas Academy (BOGAA), tare da aiwatar da tsari na tabbatar da gaskiya a biyan albashi.

    Wani babban nasara kuma shi ne kafa BOGAA a Alkaleri, cibiyar da ta samu sahalewar NBTE tare da hadin gwiwa da kamfanoni irin su Petro-Edu. Har yanzu, sama da dalibai 530 ne suka kammala karatu, yayin da gwamnatin jihar ta ware fiye da ₦6 biliyan domin gina sabon babban harabar makarantar.

    Baya ga haka, a watan Disamba 2023, aka kafa dokar Mining Consent Letter Policy, inda aka dakatar da sarakunan gargajiya daga bayar da izinin hakar ma’adinai ba tare da kulawar gwamnati ba. Wannan ya taimaka wajen dakile barna, hana ayyukan ba bisa ka’ida ba da kuma karuwar kudaden shiga.

    Ma’aikatar ta kuma fara tattara bayanan duk masu hakar ma’adinai na gargajiya tare da basu damar shiga tsarin gwamnati. Wannan ya taimaka wajen samar da ayyukan yi, karuwar kudaden shiga da kuma rage matsalolin tsaro.

    Daga shekarar 2023 zuwa yanzu, sama da kamfanoni 100 aka yi musu rijista da ma’aikatar, yayin da kudaden shiga suka tashi daga sifili zuwa miliyoyin naira a kowane wata.

    A gefe guda kuma, an kafa hadin gwiwa tsakanin BAMSEL da kamfanin Indiya Prompt Workman Ltd, da darajar sama da dala miliyan 5, domin bude cibiyar kasuwancin ma’adinai ta kasa da kasa a Bauchi.

    Babban abin da aka fi yaba shi ne jarin sama da dala biliyan 2 da aka samu a bangaren hakar ma’adinai da masana’antu. A Toro LGA, aikin $50m Rare Earth Elements Factory ya kusa kammaluwa, yayin da a Gwana, Alkaleri LGA, ake aikin gina cibiyar siminti mai darajar $1.5bn wacce za ta samar da wutar lantarki 150 MW da dubban ayyukan yi.

     A watan Mayu 2025, Hon. Bello ya jagoranci tawagar jihar zuwa babban taron hakar ma’adinai na CIM CONNECT a Montreal, Kanada, tare da wasu kasashe kamar China da Afirka ta Kudu, inda aka kara fito da Bauchi a matsayin daya daga cikin wuraren da ake sa ran samun manyan jarin kasa da kasa.

    Da yake magana, Hon. Bello ya ce:

    “Wadannan ayyuka ba wai kawai ayyukan yau da kullum ba ne, su ne ginshikan gado da za su tabbatar da makomar Bauchi a doron cigaba, dorewa da kirkire-kirkire.”

    A halin yanzu, masana harkokin ma’adinai na ganin Bauchi a matsayin jagora a fagen hakar ma’adinai a Najeriya, abin da suka danganta da hangen nesa da jagorancin Gwamna Bala Mohammed da kuma kwazon Kwamishina Maiwada Bello.
    (more…)

  • Zamani TV ta ƙaddamar da Sabon Shafin Labarai a Yanar Gizo

    Kamfanin yada labarai na Zamani TV ya ƙaddamar da sabon shafin yanar gizo na musamman domin kawo wa al’umma sahihan labarai cikin sauƙi da sauri. Wannan mataki wani ɓangare ne na ci gaba da inganta hanyoyin sadarwa da yada bayanai na zamani ga masu sauraro da masu kallo a sassa daban-daban na ƙasa da ƙetare.

    Shafin yanar gizon zai riƙa bayar da labarai kan fannoni daban-daban kamar su siyasa, tattalin arziƙi, al’adu, kiwon lafiya, wasanni, da kuma rahotanni na musamman da suka shafi rayuwar yau da kullum.

    Shugabannin kamfanin sun bayyana cewa ƙaddamar da shafin labaran ya nuna jajircewar Zamani TV wajen amfani da fasahar zamani don isar da sahihan bayanai cikin gaggawa, tare da ƙarfafa yadda matasa da sauran al’umma za su iya samun damar labarai kai tsaye ba tare da wahala ba.