Hon. Mansur Manu Soro Ya Kafa Cibiyar Karatu ta NOUN a Soro, Jihar Bauchi
Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Darazo–Ganjuwa, Hon. Mansur Manu Soro, ya kaddamar da sabuwar cibiyar karatu ta National Open University of Nigeria (NOUN) a garin Soro, Jihar Bauchi — wani babban ci gaba a fannin ilimi a yankin Bauchi da Arewa maso Gabas baki daya.
Cibiyar, wacce aka gina a fili mai fadin kusan hektar 10, tana dauke da manyan gine-gine masu inganci da za su iya karbar dalibai fiye da 1,000 a matakin digiri. Hon. Soro ya bayyana cewa wannan cibiyar ita ce irinta ta farko a duk gundumar Sanata ta Bauchi ta Tsakiya (Bauchi Central Senatorial District).
A wajen kaddamarwar, Hon. Soro ya jaddada cewa yankin Arewa maso Gabas da kuma mazabar Darazo–Ganjuwa na daga cikin wuraren da suka sha fama da wariya da sakaci wajen rabon albarkatun kasa da muhimman ayyukan raya kasa. Ya ce lokaci ya yi da za a mayar da hankali kan ilimi a matsayin hanyar ‘yanci da ci gaba.
Bude cibiyar NOUN a Soro, wacce ita ce ta farko a dukan Bauchi Central Senatorial District, na daga cikin muhimman ayyukan tarihi da muka gabatar a fannin ilimi.
Mun fara irin wannan aiki a shekarar 2021 a matakin firamare da sakandare, inda muka kafa makarantu hudu (4) na Gifted Senior Secondary Schools da kuma makarantar firamare ta musamman guda (1) a Sade, Soro, Kafin Madaki, Darazo da Lanzai.”
Hon. Soro ya kara da cewa yana da niyyar ci gaba da inganta fannin ilimi musamman a kauyuka da ke da karancin damarmaki, domin tabbatar da cewa kowanne yaro yana da damar samun ilimi mai inganci.
Ana sa ran cibiyar NOUN da ke Soro za ta fara karbar dalibai nan gaba kadan, tare da samar da damar karatu ga wadanda ba su da ikon zuwa jami.